Littafin Wakoki Hausa Hymns
Hymn 62 Ya Ubangijinmu, Kalmarka Ta Dauwama Lyrics
1
Ya Ubangijinmu, Kalmarka ta dauwama
Wajib ne a gaskata, a kuma karƃe ta.
2
Idan maƙiyanmu suna tsananta mana,
Maganar cetonka ita ce ƙarfinmu.
3
In wahala ta zo, ko masifa ta taso,
Haskenka zai bishe mu, za ya kiyaye mu.
4
Wa ya san misalin murna mafificiya
Ta miƙa bishararka zuwa mutanenka.
5
Jinƙanka ke ba da taimako ga masu rai,
Maganarka ta’aziyya ga wanda ke mutuwa.
6
Mu da muka gane tsarkin wannan Kalma,
Sai mu ƙaunace ka, don kullum mu bi ka.
