Littafin Wakoki Hausa Hymns
Hymn 161 Babban Malami Ne Ya Zo da Dare Lyrics
1
Babban malami ne ya zo da dare
A wurin Yesu don ya tambaye shi
Zancen hanyar ceto, har Yesu ya ce,
“A haife ka kuma.”
KORUS
Dole a haife ka, a sake haihuwarka,
Hakika, mai neman shiga Sama can
Dole haihuwa sau biyu.
2
Ku mutane duk, kasa kunne a nan
Ga zancen Yesu Ubangijinmu dai,
A bin da ya ce ya shafe mu duka,
“A haife ku kuma.”
Korus
3
Idan kana so ka kai wurin Allah,
Ka huta a cikin gidan daraja,
Idan kana son rai na har abada,
A haife ka kuma.
Korus
4
“Zancen nan da wuya, ba dama.” ka ce
Ka zo wurin Yesu, zai yiwu sosai
Shi yana da ikon al’ajabi fa,
Zai sake haihuwarka.
Korus