Littafin Wakoki Hausa Hymns
Hymn 488 Muna da Murna Yau Lyrics
1
Mu matan (Sunan gari
muna da murna yau, domin wanna aure, aure mai nasara
Mu yi murna mataye mu raira godiya muna yin addu’a domin wanna gida.
2
Amariya ki daɗe kina yin addu’a, kina roƙon Allah ya baki mijin aure.
Yau kin samu amarya ki yi godiya, kina yabon Allah domin Alherinsa.
3
Ango mun san daɗe kana addu’a kan roƙon Allah, ya baka macen aure.
Yau ka samu ango ka raira Halleluya, kan yabon Allan domin Alherinsa
4
Amarya ki zama kanbi ga mijinki, domin macen kirki kanbi ce ga mijinta
Kiyi masa biyayya a cikin kome duk, ki kaunace shi kamar yadda Allah ya ce.
5
Ko cikin wahala ko cikin jin daɗi, ko cikin lafiya ko a cikin kunci.
Ku kasance masu ƙaunar junanku kullum, kuna yin addu’a zaku yi nasara.
6
Samarai da ƴan mata shawar gareku, in zaku aure ku nemi nufin Allah.
Muna roƙonka, Allah amsa addu’armu, domin matasanmu ka muna ikonka.