Littafin Wakoki Hausa Hymns
Hymn 427 Isowar Yesu A Duniyan Nan Lyrics
1
Isowar Yesu a duniyan nan
Al’ummai za su ji tsoro.
Za su ce ma duwatsu da fannu,
Ɓoye mu daga fuskarsa
KORUS
Wannan ƙarshen ranar Allah ce.
Wanene za ya tsaya a ranan nan, m’m,
Ko kun tuba da toka a ranan nan, m’m,
Za a ce babu dama .
2
Za ya ce, “Na aiko Yesu Kiristi”.
Ku kun ƙi ku karƃe shi.
Kun giciye shi a bisa itace,
Domin ba ku ƙaunarsa.
Korus
3
Ni ma ranar ramawata ta zo.
Zan saka ma kowa.
Bisa gwalgwadon aikin da ya yi
Da kuma ladansa.
Korus
4
Ranan nan ba cewa, “Ya Allahmu,
Kai ka zalunce mu”,
Shi kuma za ya ce, “A’a mutane,
Ni ban zalunce ku ba “.
Korus
5
Za ku ce “Mun tubu, ya Allahmu”
Shi za ya ce, “ba dama”.
Za ku ce, “ka yafe mu, ya Allah”.
Za ya ce, “babu dama”.
Korus
6
Za ye ce “Jinin Yesu na ba da shi,
Domin zunubanku.”
Wannan ya isa domin fansarku
Ku kun ƙi bangaskiya. »
Korus
7
Na gama, na gama, kun shiga wuta nan.
Da na shirya ma Shaiɗan.
Wayyo ! Allah mun shiga azaba.
Ku kun shiga ba tausayi.
Korus