Site icon Treasure Hymns – Hausa

Hymn 262 Da Jininsa Ya Fansa, da Ransa Ne Ya Biya Lyrics

Littafin Wakoki Hausa Hymns

Hymn 262 Da Jininsa Ya Fansa, da Ransa Ne Ya Biya Lyrics

 

1
Da jininsa ya fansa, da ransa ne ya biya
Laifofin duk jama’a, bashi mai girma ne.
Ya iske mu a jeji, ya kai mu gidansa,
Ba bayi nan gaba ba, ƴaƴan sarautarsa.

2
Me ne dalilin wannan aikin al’ajabi?
Ya wuce dukan faɗi, ya zarce tunani.
Me za mu kai gare shi, shaidar godiyarmu?
Bayi ba su da zaƃi, ko da, mu nasa ne.

3
A cikin mulkin Allah, an kafa hidima.
Gare mu aka raba abin da za mu iya.
Ba domin ikon kanmu ko kuwa da karfi ba,
“Da ikon nawa Ruhu,” Ubangiji ya ce.

4
Allah Mahaliccinmu, Yesu mai ba da rai,
Ruhu mai taimakonmu, uku a cikin ɗaya, Ranmu da aka saya, aikin da mu ke yi,
Ruhunmu duk da jiki, karƃa, godiyarmu ne.

Exit mobile version