Littafin Wakoki Hausa Hymns
Hymn 129 Farkon Zuwan Almasihu Daga Sama Ne Ya Zo Lyrics
1
Farkon zuwan Almasihu daga Sama ne ya zo
Zaman neman duk mutane ƃatattu
Komawarsa ta yi kusa, ya yi zancen taimako,
Masu Binsa suna nan, ya ce da su.
KORUS
“Zuciyarku kar ta ƃaci,
Sai ku ji, ku gaskata ni.
Sama za ni gun Ubana,
Nan zan shirya muku wuri har in zo.”
2
Yesu ya yi zance cewa, “Gidan Ubana ‘na nan,
Wurin zamansa dayawa, sai in je
Don in shirya muku su, in zo in kai ku wata ran,
Inda na ke zaune fa a nan ku ke.”
Korus
3
Sake zuwan Ubangiji mu ke sauraronsa yau.
Shi alkawarinsa ba zai karya ba.
Zato babu, ba tsammani, murya tasa za mu ji.
Mai Cetonmu, ga shi, yana saukowa!
Korus
4
Kashin tsarkakansa biyu ne, matattu da masu rai.
Yesu dai zai fara ta da matattu.
Masu rai fa gaba ɗaya zai fyauce su nandanan,
Har ya sa su a wurare shiryayyu.
Korus