Littafin Wakoki Hausa Hymns
Hymn 121 Mai Cetonmu Zai Zo, Misalin Walƙiya Lyrics
1
Mai Cetonmu zai zo, misalin walƙiya,
Da ƙafon Allahnmu, lalle zai sake zuwa.
Da kiransa mai ƙarfi kuwa,
Da ikonsa zai sake zuwa.
2
Ga zancen ranan nan, tana ta zuwansa,
Ku yi ta tsaronku, ku yi ta jiransa.
Ku yi biyayya dukanku,
Ku adalai, yi shirinku.
3
Mai Cetonmu zai zo, zai amshi mulkinsa,
Numfashin bakinsa zai ci maƙiyansa.
Zai ƃaƃƃata magautansa,
Zai cinye su da ikonsa.
4
Ya Ubangiji zo, Ango Ekklesiya
Ka zo da cetonka, ka gama alkinka
Ka ji add’o’inmu yau,
Ka zo, ya Ubangiji, zo.